Sunday, July 23, 2023

Waiwaye: Ƙaruwar farashin man fetur da tuɓe hakimai shida a Bauchi...











Wannan maƙale ce da ke kawo muku muhimman batutuwan da suka faru a Najeriya cikin makon da muke bankwana da shi ranar Lahadi 16 ga watan Yuli zuwa Asabar 22 ga wata.

Farashin litar man fetur ya tashi zuwa naira 617 a Najeriya


A ranar Talata, ba zato babu tsammani ƴan Najeriya suka tashi da labarin ƙarin farashin man fetur a faɗin ƙasar.

Farashin litar man fetur ya kai naira 617 a sassan ƙasar, ƙari a kan 540 da aka saba sayarwa a baya.

A jawabinsa na karɓar mulki, shugaban ƙasar, Bola Tinubu ya sanar da cire tallafin man fetur, lamarin da ya ingiza farashin litar man daga kimanin naira 200 zuwa naira 600.

Cire tallafin man fetur dai na nufin za a riƙa samun hawa da saukar farashin litar mai domin kuwa kasuwa ce za ta tantance farashin.

Kuma hakan na nufin ƴan kasuwa za su iya shigar da man fetur daga ƙasashen waje kuma su sayar a farashin da suke so ta yadda za su mayar da uwar kuɗi kuma su samu riba.

Tun bayan cire tallafin man fetur ɗin farashin sufuri da kayan masarufi ya riƙa hauhawa.

Lamarin da ya sanya gwamnatin ƙasar ta ce za ta fito da wasu shirye-shiryen da za su sauƙaƙa wa mutane raɗaɗin cire tallafin.

Ku shiga nan don karanta cikakken labarin



Shugaban Najeriya Bora Ahemd Tinubu ya amince ca kafa asusun gina ababen more rayuwa a jihohin ƙasar 36, a wani mataki na rage wa yan ƙasar raɗaɗin cire tarafın man fetur.

Shugaban ya amince da matakin ne a lokacin taron wata-wata na kwamitin kula da asusun raba kuɗin shiga na gwamnatin ƙasar (FAAC) da aka gudanar ranar Alhamis a Abuja.

Cikin wata sanarwa da mai magana da yawun shugaban ƙasar Dele Alake ya fitar, ya ce sabon asusun zai taimaka wa jihohin ƙasar wajen zuba jari a ɓangarorin sufuri da harkokin noma da gina tituna da kasuwanni da kiwon dabbobi da ɓangaren lafiya da ilimi musamman a matakin farko, da wutar lantarki da ruwan sha domin haɓaka tattalin arzki da samar da ayyukan yi ga ƴan ƙasar.

Kwamitin ya kuma amince da ajiye wani ɓangare na kuɗin da ake rabawa a kowane wata domin takaita tasirin aeruwar shiga da za a iya samu sakamakon matakan cire tallatin mai da daidata farashin dala tare da hauhawar farashin kayayyaki za su iya haifarwa.

Kwamitin ya ce daga cikin naira tiliyan 1.9 na kuɗin shigar da aka samu a watan Yunin 2023, naira biliyan 907 ne kawai za a raba tsakanin matakan gwamnatin ƙasar uku, yayin da za a ajiye naira biliyan 790 a asusun.

Waɗannan kuɗaɗen da za a riƙa ajiyewa za su taimaka wajen samar da asusun gina ababen more rayuwa tare da aiwatar da wasu abubuwa, domin tabbatar da an yi amfani da kuɗin tallafin wajen gina muhimman abubuwan ci gaba, domin inganta rayuwar yan ƙasar kamar yadda sanarwar ta bayyana.

Haka kuma kwamitin ya yaba wa shugaban ƙasar bisa matakin cire tallafin man tare da ɓullo da matakai daban-daban na tallafa wa 'yan ƙasar domin rage masu raɗaɗin cire tallafin.

Shugaban jam'iyyar APC mai mulkin Najeriya, Sanata Abdullahi Adamu ya ajiye mukaminsa bayan kwashe shekara ɗaya da 'yan watanni yana jagorantar jam'iyyar.

Sabon shugaban riƙo na jam'iyyar, Sanata Abubakar Kyari ne ya tabbabar da murabus ɗin Adamu kwana guda bayan kafafen yaɗa labarai a Najeriya suka wallafa labarin cewa rashin jituwa tsakanin Sanata Adamu da shugaba Tinubu ya tursasa masa yar da ƙwallon mangwaro

Shugaban jam’iyyar ta APC ya bar muƙamin ne kimanin wata biyar bayan ya jagorance ta a zaɓen shugaban ƙasar, inda ta yi nasara.

Bayanai sun ce Adamu ya ajiye aikin ne tare da sakataren jam’iyyar na ƙasa, Sanata Iyiola Omisore.

Akwai dai alamu na cewa an dinga samun takun-saka a cikin jam’iyyar tun bayan da shugaba Tinubu ya kama mulki, kimanin watanni biyu da suka gabata.

Ajiye muƙamin shugaban jam’iyyar zai iya alamta cewa akwai wani babban rikici ne tsakanin ƴaƴan jam'iyyar da aka kasa samun masllaha.

Shugaban riƙon jam’iyyar na ƙasa, Abubakar Kyari ya ce Sanata Adamu bai bayyana dalilin ajiye muƙamin nasa ba.

Ku shiga nan domin karanta cikakken labarin

Gwamnatin Bauchi ta sanar da tuɓe masu sarauta shida a jihar

0 Comments:

Post a Comment

Subscribe to Post Comments [Atom]

<< Home