Sunday, October 15, 2023

KADAN DAGA CIKIN ILLOLIN RASHIN YIN AURE..


















KADAN DAGA CIKIN ILLOLIN RASHIN YIN AURE.. 

Manzon Allah (S) Yana Cewa: "Mafiya Yawan 'Yan Wuta Gwagware ne, a Wani Wajen Kuma Yace: "Zababbun al'umma ta sune masu iyali, ashararan al'umma ta kuma (mafiya yawa) gwagware ne."

A cikin Alkafiy, daga Annabi (S) Yace: "Wanda Ya yi aure, to ya Cimma rabin addininsa, Sai ya ji tsoron Allah a cikin ragowar (cikon addinin).

Manzon Allah (S) Yace: "Wanda Yake So Ya sadu da Allah Yana tsarkakakke, to ya je gare shi alhali yana da aure."

A cikin Attahzib, daga Manzon Allah (S) Yace: "Wulakantattun matattunku sune gwagware."

Na so na takaita Wannan rubutun anan, amma saboda ina son na kwadaitar daku sannan na tsoratar daku kan al'amarin aure.

An ruwaito daga Imam Sadiq (AS) Yana cewa: "Duk wanda ya aurar da gwauro (ko garuruwa) zai kasance daga cikin Wadanda Allah zai yi duba da Rahamarsa a ranar Alkiyama.

Imam Jawad (as) Yace: "Wanda Ya Nema auren 'Yar ku Kuma kuka yarda da riko da addininsa da kuma amanarsa to ku aura masa.

Wata rana Wani Mutum Yazo wajen Imam Husain (as) Yace "Ya Imam Ina da 'Ya, Wa kake ganin zan aurar da ita ga shi? Sai Imam (as) Yace Masa: "Ka aurar da ita ga Wanda Yake tsoron Allah ta'ala, Saboda shi mai tsoron Allah idan Yana son ta zai girmama ta, idan kuwa ta fusata shi ba zai zalunce ta ba.

Imam Sadik (as) Yace: "Wanda Ya auri Mace Saboda dukiyar ta, Allah zai kyale shi da dukiyar."

Manzon Allah (S) Yace: Wanda ya auri Mace kawai Saboda Kyawunta, a karshe ba zai ga abin da Yake so ko yake sha'awa a tare da ita ba.
Wanda kuwa Ya auri mace don Dukiyarta Allah zai bar shi da Dukiyar. don haka na hore ku da neman Ma'abociyar addini.

Muna rokon ta'ala ya azurta mu da abokan zama nagari ma'abota addini.

0 Comments:

Post a Comment

Subscribe to Post Comments [Atom]

<< Home