Thursday, August 31, 2023

JUYIN MULKIN GABON: Tinubu ya ce 'annobar ƙarfa-ƙarfa' ce ke bazuwa cikin Afrika











A ranar Asabar ce aka yi zaɓen shugaban ƙasa a gaban, wanda ya haifar da ruɗani, bayan an bayyana cewa Shugaba Ali Bongo ne ya yi nasara a zangon mulkin sa na uku a jere.

Ali Bongo ya zama tun cikin 2009, bayan mutuwar mahaifin sa, Omar Bango.

A zaɓen ranar Asabar, Hukumar Zaɓen Gabon ta ce Ali Bango ya samu kashi 64.27 na yawan ƙuri’un da aka kaɗa. Amma ɗan adawar sa Albert Ondo Ossa ya samu kashi 30.77.” An dai ɗauki tsawon lokaci ana kunge-kunge kafin a bayyana sakamakon zaɓen.

Rahotanni sun ce an ji ƙararrakin harbin bindiga a babban birnin Gabon, Libreville. Kuma ba a san inda shugaban ƙasar ya ke ko halin da ya ke ciki ba.

Juyin mulkin ya zo wata ɗaya daidai bayan juyin mulkin Nijar. Kuma mako ɗaya bayan AU ta kafa wa Sojojin Mulkin Nijar takunkumi, tare da dakatar da ƙasar daga kasancewar ta mamba a AU.





A ranar Asabar ce aka yi zaɓen shugaban ƙasa a gaban, wanda ya haifar da ruɗani, bayan an bayyana cewa Shugaba Ali Bongo ne ya yi nasara a zangon mulkin sa na uku a jere.


Ali Bongo ya zama tun cikin 2009, bayan mutuwar mahaifin sa, Omar Bango.


A zaɓen ranar Asabar, Hukumar Zaɓen Gabon ta ce Ali Bango ya samu kashi 64.27 na yawan ƙuri’un da aka kaɗa. Amma ɗan adawar sa Albert Ondo Ossa ya samu kashi 30.77.” An dai ɗauki tsawon lokaci ana kunge-kunge kafin a bayyana sakamakon zaɓen.


Rahotanni sun ce an ji ƙararrakin harbin bindiga a babban birnin Gabon, Libreville. Kuma ba a san inda shugaban ƙasar ya ke ko halin da ya ke ciki ba.

Juyin mulkin ya zo wata ɗaya daidai bayan juyin mulkin Nijar. Kuma mako ɗaya bayan AU ta kafa wa Sojojin Mulkin Nijar takunkumi, tare da dakatar da ƙasar daga kasancewar ta mamba a AU.

0 Comments:

Post a Comment

Subscribe to Post Comments [Atom]

<< Home