Thursday, February 22, 2024

YANZU-YANZU: Ɓatagari sun daka wawa kan tireloli ɗauke da kayan abinci a jihar Neja












Rahotanni da ga jihar Neja na baiyana cewa wasu ɓatagari sun tare tireloli makil da kayan abinci da kayan abinci a yankin Suleja, lamarin da ya sa sojoji suka yi harbi sama don korar su a yau Alhamis.

Wani ganau, Alhassan Abdullahi, ya shaida wa wakilin Daily Trust cewa ɓatagarin, wanda suka kona tayoyi sun tare tirelolin da ke tahowa daga Abuja zuwa Kaduna.

Ya ce sun sace buhunan kayan abinci iri-iri, musamman shinkafa kafin sojoji su isa wurin.

“Allah Ya sanya sojoji sun isa wurin sannan suka fara harbin bindiga a iska don tsoratar da ɓatagarin. Amma ko da hakan, da yawa daga cikinsu sun tafi da buhunan shinkafa da katan-katan na taliya da sauran kayan abinci.”

Wannan ci gaban dai na zuwa ne a daidai lokacin da ake fama da wahalhalun da kasar ke fama da shi wanda ya haifar da zanga-zanga a sassa daban-daban na kasar.

0 Comments:

Post a Comment

Subscribe to Post Comments [Atom]

<< Home