Tuesday, February 6, 2024

Ana zargin wata amarya da yanke makarfafar angonta bayan da ta fara sumar da shi da Tabarya











Tunda fari dai amaryar ta bukaci angon nata da ya siyo mata Madara ne bayan da ya dawo daga wajen sana’anarsa ta saran Itace a Jeji, lamarin da yasa ya je siyar da itacen bai siyu, inda ya ranto kudi ya siyo ya kawo mata, dan haka ta bukaci ya rakata bakin Labi ta tsinko ganyen Magani, ashe ta boye Tabarya da wuka a Hijabi.

Dala fm sun ruwaito cewa, suna zuwa bakin labi gurin da babu mutane kawai sai yaji ta kwantare masa Kai da tabaryar ta baya har ta kai ta karya masa Mumamuki ta zubar masa da Hakora ya suma, daga nan akayi zargin ta zaro wukar inda ta yankesu ta saka su a Leda.

Bayan da asirinta ya tonu ne aka kai ta wajen ‘yan sanda, inda a yanzu shi kuma yake kwance a Asibitin koyarwa na Mallam Aminu kano, sai dai likitoci sun ce idan ma ya rayu to babu zancen Makarfafar domin yanzu haka ta riga ta rube a ledar har an binne ta

A zantawar wakilinmu Ibrahim Abdullahi sorondinki da ‘yar-uwar angon Zulaihat Muhammad ta ce, auren zumunci aka yi musu, kasancewar iyayen angon mai suna Sa’idu Lawal ‘yan uwan iyayen amaryar ne.

Ta kuma ce yanzu haka amaryar da ake zargin ta na hannun mahukunta a jihar Kaduna, inda al’amarin ya faru a garin Tafa har zuwa aga abun da hali zai yi dangane da jikin angon na ta idan ya rayu, kasancewar kwanaki 12 da yin bikinsu al’amarin ya faru.

0 Comments:

Post a Comment

Subscribe to Post Comments [Atom]

<< Home