Friday, June 23, 2023

Rashin Tsaro: ‘Yan Bindiga Sun Yi Garkuwa Da Wata Mata Manajar Banki, Sun Dade Suna Yi Mata Gargadi.

Rashin Tsaro: ‘Yan Bindiga Sun Yi Garkuwa Da Wata Mata Manajar Banki, Sun Dade Suna Yi Mata Gargadi.












Masu garkuwa sun sace wata manajar daya cikin bankunan Najeriya a akan hanyar Sani Abacha daf kwanan PDP a birnin Yenagoa.



Wanda aka sacen, Nneka Unoka Ugonochie ta na kan hanyarta na zuwa aiki ne lokacin da ‘yan bindigan suka kama ta.

‘Yan bindigan sun yi shigar bultu da kayan sojoji lokacin da suka sace manajar bankin a daidai inda jami’an tsaro suke tsayuwa.



Jihar Bayelsa – ‘Yan bingiga sun yi garkuwa da wata manajar banki a Najeriya Mrs Nneka Unoka Ugonochie a jihar Bayelsa.

Lamarin ya faru ne a ranar Juma’a 16 ga watan Yuni a kan hanyar Sani Abacha da ke birnin Yenagoa.


Daily Trust ta tattaro cewa lamarin ya ba wa mutane mamaki ganin yadda da jami’an tsaro ke zube a wurin amma suka samu damar sace matar.

Wata majiya ta tabbatar cewa ‘yan bindigan sun dade suna yi wa matar kashedi akan cewa ta kaura daga gidanta wanda ke kusa da gidan mai gidansu da aka kama.


The Nation ta tabbatar cewa a baya gamayyar jami’an tsaro ne ke gadin matar kafin daga baya su watse saboda korafi daga matar na tsadar daukar nauyinsu.

An gargadi matar sau da dama akan cewa dole ta zauna cikin shirin ko ta kwana har sai lokacin da gwamnati ta kwace gidan shugaban masu garkuwan.



0 Comments:

Post a Comment

Subscribe to Post Comments [Atom]

<< Home